Amurka Ta Umarci ‘Yan Kasarta Su Fice Daga Iraki Nan Take Saboda Barazanar Tsaro

uploads/images/newsimages/KatsinaTimes15032026_140930_Tramp_mirotvorac_napado_sedam_zemalja.jpg


KatsinaTimes 

Gwamnatin Amurka ta bukaci dukkan ‘yan kasarta da ma’aikatanta da ke zaune a Iraki da su gaggauta barin kasar nan take, sakamakon karuwar barazanar tsaro da ake dangantawa da da kasar Iran.

Wannan gargadi ya zo ne bayan rahotannin jami’an tsaron Iraki da suka tabbatar da cewa wani makami mai linzami ya fadi a harabar ofishin jakadancin Amurka da ke birnin Bagadaza. Rahotanni sun nuna cewa makamin ya afka kusa da filin saukar jirage masu saukar ungulu (helipad) a cikin harabar jakadancin, lamarin da ya haddasa gobara a saman rufin ginin.

A cikin wata sanarwa da gwamnatin Amurka ta fitar, ta bayyana cewa kungiyoyin mayakan da ke da alaka da Iran sun zama babbar barazana ga tsaron jama’a a Iraki. Sanarwar ta kara da cewa wadannan kungiyoyi sun kai hare-hare kan ‘yan Amurka, cibiyoyin diflomasiyya na Amurka, kasuwanci da kuma muhimman kayayyakin more rayuwa, musamman wadanda Amurka ke gudanarwa a bangaren makamashi.

Har ila yau, an bayyana cewa kungiyoyin mayakan sun kai hare-hare kan otel-otel da baki ‘yan kasashen waje ke sauka, tare da wasu wurare da ke da alaka da Amurka a sassa daban-daban na Iraki.

Sanarwar ta kuma yi gargadin cewa ‘yan Amurka na fuskantar hadarin sace-sace, inda aka ce wasu daga cikinsu sun taba zama hari kai tsaye ga wadannan kungiyoyi. Haka kuma an nuna damuwa cewa irin wadannan kungiyoyi na iya hana hukumomin Iraki damar daukar matakan gaggawa yadda ya kamata idan wata matsala ta taso.

Sakamakon haka, gwamnatin Amurka ta sanya Iraki a matakin gargadin tafiya na Level 4, wanda shi ne mafi girman matakin hadarin tsaro, tare da sake nanata cewa dukkan ‘yan Amurka su gaggauta ficewa daga kasar.

A cewar sanarwar, gwamnatin Amurka za ta taimaka wajen saukaka hanyoyin fitar da ‘yan kasarta daga Iraki ga duk wanda ke son barin kasar cikin gaggawa.

Follow Us